Kungiyar likitoci a Najeriya na fuskantar rashin yawan ma'aikata
Likita daya kacal ne ke kula da kimani marasa lafiya 6,000 a Najeriya. Kungiyar na fuskantar rashin yawan ma'aikata.
Kungiyar kiwon lafiya ta duniya, WHO ta ce kowani likita a Najeriya na kula da kimani marasa lafiya guda 6,000.
Farfesa
Titus Ibekwe, shugaban sashen kunnen, hanci da makogwaro (ENT) ta
Jami'ar Abuja, babban birnin tarayya ya bayyana wannan a ranar
Laraba,25 ga watan Janairu.
Farfesa Ibekwe ya ce wannan gibin
na da hadari matuka ga kiwon lafiya a kasar. Farfesa wanda shi ne kuma
tsohon mataimakin shugaban Kungiyar likitocin (NMA) a Najeriya, ya
bayyana cewa ma'aikata likita a Nigeria na fuskanta wata masala ta kula
yawan marasa lafiya.
Farfesa ya na
cewa mafi yawa cikin kayan aikin kiwon lafiya a wurare daban-daban a
kasar suna bukatan kula da kuma maye gurbin su da kayan aiki na zamani.
Ya
ce, a yanzu aka, kasar Najeriya ta na gurbi na 187th daga 191 a
didigan kungiyar kiwon lafiya ta duniya, WHO a gurbin sauran kasashen.
Kungiyar
kiwon lafiya ta duniya, WHO ta bayar da shawara cewa mafi karanci
likita daya ya halarci marasa lafiya 600 amma wannan shawara ta samu
wata salo a Najeriya a inda likita daya na kula da kimani marasa lafiya
6,000.
A halin yanzu, likitoci a
karkashin wata kungiyar NMA sun koka a kan igantace kaiyakin aiki a
wurare a kasar, yayin da kuma suka yi tir da shugaba Muhammadu Buhari da
kuma sauran jigon jami'an gwamnati domin neman kiwon lafiya a kasashen
waje.
Ku kasance tare da mu
Comments